• About
  • Contact
Tuesday, June 17, 2025
  • Login
Ibrahim Sheme
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
No Result
View All Result
Ibrahim Sheme
No Result
View All Result
Home Da Hausa

Bugu Da Guduma

IBRAHIM SHEME by IBRAHIM SHEME
August 26, 2012
in Da Hausa
0

 

Allah na, ya sarki gwani,

Roƙo naka yi zan soma.

 

Buɗe mini tagar zurfafa-

War ƙwalwa, ban ilhama.

 

Domin manzon ka Ahmadu,

Wannan ɗan hannun dama.

 

Don Dija uwar duka muminai,

Don Zainab bint Khuzaima.

 

Wannan matan na Muhammadu,

Ar-Rasul hannun sa na kama.

 

Wani ja’iru ɗan ɗan karuwai,

Shi ne ya taɓo ne da kima.

 

Wai ya riƙe gurnati har da bam,

To gu nai ba ni da girma.

 

Shawaraki zo zauna ka ji,

Koli na za ni baje ma.

 

Ka ɗauka na manta da kai?

Ho takari da babu igama!

 

Yau sam sam lallai ba ragi,

Wallai ni sai na rama.

 

Dundu da gula zan yi maka,

Ga ƙusa za ni buga ma.

 

Kai tashi da mugun gyangyaɗi,

Sabon saƙo zan yi ma.

 

Yasin ce zan jawo maka,

Alƙunut kai har ma Amma.

 

Ko ko dai baiti ’yan kaɗan,

Babban gyambo in fama?

 

Ɓarawo ne na ƙwaƙwalwa,

Nomau ɗan Sarkin Noma!

 

A kwatar can nats tsamo ka,

Wawan kai sai kak koma.

 

Na ba ka kuɗi har fam ɗari

Jari, ga shanun noma.

 

Su ne ka kaɗar ga kilakilai,

Ka koma dogon hamma.

 

Kullum zagin mu cikin gari,

Harshe ya kai mil goma.

 

Kullum sara ta ɗai kake,

Ni gamji ina daɗa girma.

 

To ganye ne kaka sassabe,

Ni tushe na bai suma.

 

Na gode Allah Rahimi,

Duniyar nan na sha fama.

 

Yau ga ni garas kuma tangaran,

Ƙarfi ma yanzu na soma.

 

Farkar ka a ran nan ta dafa

Maka girki, oh tai himma!

 

Ta ba ka tuwo ka nannaga,

Wulli mai babbar loma.

 

Soyen alade ta buga maka,

Ta ba ka da dambun nama.

 

Ka take cikin ka da burkutu,

Ka ɗauka koko ta dama!

 

Sarkin kwaɗayi, mai kwarmato,

Doki mai ƙarnin nama.

 

Kai ba ka aboki yanzu mai

Sallah, sai arnan Koma.

 

Wawan sarki ba ka da kai,

Ɓutal, gyandai, camama.

 

Sannun ka da ƙaryar arziki,

Banza kullum sai homa.

 

Bayahude lallai ka riƙa,

Wai kai yau babu hukuma.

 

Dolo har yau ba ka kintsu ba,

Kai kullum ka sha mama.

 

Bunsuru mai neman ’ya tasa,

Domin kai ba ka iƙama.

 

Mai danne yara ƙanƙana,

Da uwar ma in ka ga dama.

 

Ba jinƙai, mugun makiri?

Ka zambaci hatta umma.

 

Mai laifi ba ka da karsashi,

Ɗan sanda kai yak kama.

 

Kai tusa, warin ya bugo

Daga Legas ya kai Bama.

 

Izzar ka ta ja maka zunguri,

Ga tarko na ya kama.

 

Je tuba ka daina haɗin faɗa,

In ka ƙi mu dinga husuma.

 

Yaƙin biro kuma ni da kai,

To yanzu ka san na soma.

 

Sunan ka mance? Iro ne,

Ko ‘Sheme bugu da guduma’.

 

Mai horon arna jiddadum,

To yau dai kan ka na koma.

 

Dangi na ku na gaida ku,

Addu’a a gare ku na nema.

 

Aikin da nake kun taimaka,

Hannu kun sa kun tama.

 

Ƙyale ni na harbi haƙarƙarin

Mugu mai sato nama.

 

Zan karya wuyan azzalumi,

Kun san ni da zafin nama.

 

Ƙarshe nan ni roƙo na yi,

Ya Jallah ka ba ni in kama,

 

Igiyar nan ta Islamiyya,

Na tuba gare ka na koma.

 

Baitin waƙar mu guda biyar,

Sai ku tara har sau goma.

 

TAMAT

26 ga Agusta, 2012

Loading

Share this:

  • Facebook
  • X

Like this:

Like Loading...
Previous Post

Ƙalubale Ga Aminu Ala

Next Post

Aron Fitila Ga Marubuta

Next Post

Aron Fitila Ga Marubuta

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • Wale Okediran @ 70: Tribute to a Workaholic Writer
  • ‘Found in Translation: Writing in Indigenous Languages’
  • Motherland at 64
  • Cikar Shehu Ɗahiru Usman Bauchi shekara 100
  • Wanda Ba Ya Fushi Da Yin Allah

Recent Comments

  1. UMAR IBRAHIM ABDULLAHI on Ta’aziyyar Hajiya Saratu Giɗaɗo (Daso) a Ranar Arba’in
Ibrahim Sheme No. 19, Chelsea Chibuzor Street, Katampe District Abuja, FCT Nigeria 📞 +234 0809 400 0071 (text) ✉️ ibrahimsheme@gmail.com
  • Home
  • About
  • Contact

© 2023 Ibrahim Sheme

No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings

© 2023 Ibrahim Sheme

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
%d