Salam. Jiya na ce zan yi wa Aminu Ladan (Alan Waƙa) wani ƙalubale. Na san za ku ce kun ji shiru. To a yau ga shi na kawo muku. Sai a karanta da haƙuri; kun san abin ‘yan koyo (dariya da ƙwalla). Kuma don Allah sha’irai a yi mini gyara.
ƘALUBALE GA AMINU ALA
Bismillah zati tsarkaka na gun ka,
Buɗan ƙwaƙwalwa baitika in shirya.
Nai dogaro a gare ka neman sa’a,
Allah Ta’ala wanda bai tarayya.
Ƙaro salati gun sa hasken haskaka,
Manzo na Dija cikamakin anbiyya.
Na yo salati har dubu kuma sau dubu,
Tsira ga Mamman wanda bai fariya.
Wannan da yai yaƙi da fir’aunoni,
Ya karya dukkan gunkunan jahiliyya.
Tsira, aminci Rabbana ka isar masa,
Manzo gare shi a kullu na yi biyayya.
Saƙon sa ya zo ne a babban kundi,
Komai da ke ciki ba ni yin jayayya.
Wani ɗan mafarki ne yake cizo na,
Ala nake neman ya yo alfiyya.
Ala Aminu da ke Kanawan Dabo,
Sarki uban ‘ya’yan da ke ƙafiyya.
Waƙa yana yi tai dubu na ƙirgo,
Duk wanda ya ce a’a shi yai ƙarya.
Kullum yaƙini nai ya wargaza zalumai,
Yaƙi yake da halin mu Najeriyya.
Tauhid a ilmu nasa Abban Husna,
Mugun halin mu da shi yake ƙiyayya.
Biron sa ga kaifi, da ya zaro shi,
Wane takobi in yana gogayya.
Duk ya karaɗe lunguna da jihadi,
Bakin shi bai hutu wajen ilmiyya.
Daddyn su ‘yanbiyu fasihul zamani,
Baban Sa’adatu, Rabbu yai sakayya.
Duka baitukan Ala akwai su a rediyo,
Kuma mun karanta darasin mun koya.
Amma mu duba ƙanƙana ne galiban,
Bai yin awa ɗaya sai ya ce ya tsaya.
Ala ka karkaɗe kunnuwa domin ka ji,
Roƙo nake, Allah ya sa ka shirya.
Lallai fa aikin nan da ke hannun ka,
Har yau da saura, sai ka ɗauro niyya.
Takun ka yai nisa uban Muhsinu,
Amma su Rumi sun yi ma tserayya.
Ban ce a dole ka zam kamar Bin Malik,
Ko ko a ce kai ne gaban su ba manya.
Lallai su Rumi sun yi ma nisa a nan,
Sai kai shiri domin ka kamo hanya.
Hau taguwar ka da tsikari ya fasihu,
Keto hazon daji cire gajiyya.
Azama kake Ala a kan alƙaluma,
Domin ka zano baituka ba jinya.
Tabbas jiran ka muke amon ta ka kunno
Sauti dubu, baiti dubun alfiyya.
Ƙalubale ne ga shi nan na harbo,
Cene da ni ‘cas’ ka ji mai alkunya!
Sabon bajinta ne nake ta kira ka yi,
In ka ƙiya tilas in ɗauko lauya.
In dai ka kasa zan yi kukan kura,
In ce Kanawa kar su ‘yam ma miya.
Suna a ƙarshe Sheme ne Burhama,
Yaro makoyi, sallama kulliya.
Asali ƙasar mu ta Dikko ɗakin kara,
Amma Abuja nai zaman tarayya.
Hamdan kasiran ga ni nan na sauko
Daga mumbarin saƙon kiran alfiyya.
Baiti talatin ne a wannan waƙa,
Ƙaro guda huɗu maganin jayayya.
Ya Jallah sa Ala ya ɗau aniyya,
Domin darajar Ɗaha mai Safiyya.
Allah daɗo tsirar Rasulu ka ƙara,
Amin da amin Jallah na dasa aya.
TAMAT WA BIHAMDIL LAH
31 ga Yuli, 2012