• About
  • Contact
Thursday, July 31, 2025
  • Login
Ibrahim Sheme
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
No Result
View All Result
Ibrahim Sheme
No Result
View All Result
Home Da Hausa Waƙa

Ta’aziyyar Hajiya Saratu Giɗaɗo (Daso) a Ranar Arba’in

IBRAHIM SHEME by IBRAHIM SHEME
May 19, 2024
in Waƙa
1
Ta’aziyyar Hajiya Saratu Giɗaɗo (Daso) a Ranar Arba’in
Marigayiya Hajiya Saratu Giɗaɗo (Daso)

Marigayiya Hajiya Saratu Giɗaɗo (Daso)

TA’AZIYYAR HAJIYA SARATU GIƊAƊO (DASO) A RANAR ARBA’IN

Daga Ibrahim Sheme

1. Al-Mujibu ka ba ni tanyo,
Zantuka domin in shiryo,
Ba gwaninta ai a koyo,
Addu’a ce za ni ɗan yo,
Ta rashin ‘yar’uwar mu Daso.

2. Gaisuwa ta ta taƙaita,
Gun mafificin halitta,
Ɗaha mai zurfin fahimta,
Ɗan Amina uba ga Binta,
Wanda tai ƙaunar sa Daso.

3. Mutuwa mai wafce kaɗo,
‘Yar Fulani ce ta fyaɗo,
Saratun mu ɗiyar Giɗaɗo,
Ba sanarwa ta saɗaɗo,
Ta yi wuf da ƙawar mu Daso.

4. Saratun mu ɗiyar Muhamman,
‘Yar Kano ce ita wannan,
Jaruma a Kannywood sannan,
Ayyukan ta a duniyar nan,
Sun yi tasiri da naso.

5. Tun da farko rayuwar ta,
Ta yi ticin makaranta,
‘Yan firamare fa mata,
Har mazan duk ta ƙagauta,
Gun batun koyon su, Daso.

6. Sai ta tsoma ƙafa a harkar
Shirya fim ku ji don ku sadar,
Kamfanin su Sarauniya har,
Masu barci duk ta farkar,
Masu so har wanda bai so.

7. Tai fice a finafinan mu,
Mun gani a akwatunan mu,
Can ta hasko rayuwar mu,
Dariya ta saka a ran mu,
In tana aktin ta Daso.

8. Masu fim kaf ba kamar ta,
In mugunta suka sa ta,
Kishiya ko ko uwar ta,
Za ta yi shi iya gwaninta,
Yadda daraktan ta ke so.

9. Shi fa rol in dai ta taka,
In na kirki babu shakka,
Ko na assha ne ta tafka,
Sai a ce, “Allah ya saka,
Ya biya burin ki Daso.”

10. Ban da fim ɗin, kar ku manta,
Gun ciyarwa kun fa san ta,
Tallafin duk mai buƙata,
Yara, tsofaffi da mata,
Ko a nan lada ta kwaso.

11. Tai rabo na ruwa, abinci,
Masu so a gare ta sun ci,
Ga tufafi – har ga zuci –
Ta kira mai shara barci:
“In kana so, to ka taso.”

12. Ran da Ramadan ya ƙare,
Malamai suka ce a daure,
Ai talatin kar a sare,
Shi ta ɗauka don ta more,
Don cikar ladar ta Daso.

13. Tai shirin Sallah da maiƙo,
To ashe da akwai fa saƙo,
Ba daɗewa ta yi baƙo,
Ran ta ne aka ce ya miƙo,
Ya taho, haka Hayyu ke so.

14. Tai sahur, sallah, ta kwanta,
Sai ta ce, “Bari dai na huta,”
Rabbana ya katse zaman ta,
Can da hantsi ‘yar’uwar ta,
Tai kira, ai ba ta taso.

15. Duk gari kowa ya ruɗe,
Zuciyoyi suka bauɗe,
Lamarin jama’a ya cuɗe,
Duk kalar kowa ta koɗe,
Ko zuma ma ba ta laso.

16. Duk masoya sun saduda,
Dandazon jama’a mashaida,
Sun yi sallar ta a Fada,
Daga nan tafiya ta ida
Gun kushewa tata Daso.

17. An rufe ta ana ta kuka,
Turbuɗe ta akai a laka,
Zuciyoyi na ta duka,
Sai du’a’i ke ta sauka:
“Al-Gaffar yafe wa Daso!”

18. Na yi kuka har a ƙalbi,
Na siƙe a wajen jawabi,
Nai diƙin a wannan babi,
Ba ni don in wanke gurbi:
Sabulu da ruwa da soso.

19. Addu’ar mu tutur gare ta:
Zuljalalu ka jiƙan ta,
Baɗinin ta da zahirin ta,
Yafe dukkan kurakuran ta,
Sa ta Aljannar ka, Daso.

20. Muna ta roƙo gun Ta’ala:
Yafe laifukkan ta Jallah,
Kuskuren da ita ta ƙulla,
Don cikar azumi da sallah,
Ba ta duk rahamar ka, Daso.

21. Arba’in yau tun rashin ta,
Mun yi jimami a kan ta,
Gaisuwar mu ga ‘yan’uwan ta,
Har da ‘yan Kannywood zumun ta,
Don rashin sistar su, Daso.

22. Malamai ai sun ishara:
Yadda Maiduka duk ya tsara,
Ba tsimi kuma ba dabara,
Ƙaddara ce babu gyara,
Sai abin da Ƙahharu ke so.

23. Mu da ke nan ba mu kuri,
Duk daɗewa ko ko sauri,
Ko da rama ko da kauri,
Ko da zaƙi ko da bauri,
Za mu je mu ishe ta Daso.

24. Wagga waƙar ba bajinta,
Iro ɗan Mamman ya yi ta,
Sheme mai Binta da Binta,
Har ku sa Auta ta Mata,
Addu’a ce don ta Daso.

25. Baituka ashirin na jera,
Sai biyar a sama na ƙara,
Don cikar roƙon Tabara,
Na yi roƙon ba gadara,
Don biɗar rahama ga Daso.

Alhamdu lillahi!

19/05/2024

Marigayiya Hajiya Saratu Giɗaɗo (Daso) … ta cika kwana 40 da rasuwa

Loading

Share this:

  • Facebook
  • X

Like this:

Like Loading...
Tags: rasuwaSaratu Giɗaɗo Dasota'aziyya
Previous Post

Aburaɗi

Next Post

Wanda Ba Ya Fushi Da Yin Allah

Next Post
Wanda Ba Ya Fushi Da Yin Allah

Wanda Ba Ya Fushi Da Yin Allah

Comments 1

  1. UMAR IBRAHIM ABDULLAHI says:
    1 year ago

    ALLAH YAJIKANTA DA GAFARA MUKUMA ALLAH YASA MUCIKA DA IMANI

    Reply

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • Bature Tanimu Gagare: Fighting, Not Just With His Pen
  • Goron Sallah
  • Wale Okediran @ 70: Tribute to a Workaholic Writer
  • ‘Found in Translation: Writing in Indigenous Languages’
  • Motherland at 64

Recent Comments

  1. UMAR IBRAHIM ABDULLAHI on Ta’aziyyar Hajiya Saratu Giɗaɗo (Daso) a Ranar Arba’in
Ibrahim Sheme No. 19, Chelsea Chibuzor Street, Katampe District Abuja, FCT Nigeria 📞 +234 0809 400 0071 (text) ✉️ ibrahimsheme@gmail.com
  • Home
  • About
  • Contact

© 2023 Ibrahim Sheme

No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings

© 2023 Ibrahim Sheme

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
 

Loading Comments...
 

    %d