Bismilla yau ma na taho,
Taswira zan ɗan zana.
Ya Jallah ka ba ni tagomashi,
Da basira don na zauna.
Yi salatin angon A’isha,
Ni gun sa na karkata so na.
Matsalar marubuta ‘yan’uwa,
Zan sa yatsa in nuna.
Marubuta ku ni ka tausayi,
Na fara shirin in daina!
Don kun ƙi tiyatar maganin
Ciwon da yake muku ɓarna.
A sana’ar kun gaza warware
Babbar illa mummuna.
A rubutu kun gaza ci-gaba,
Wayyo, ku ‘ya’yan ANA!
‘Ya’yan HAF, sauran ma haɗo,
Ogogin har da ƙanana.
Kaicon ku haɗin kai kun gaza,
Wallen ku na gan shi a rana.
Shi yas sa ba kwa kasuwa,
Gwandar ku tana ƙin nuna.
Haske a gida bai samuwa,
Lantarki sai an jona.
Dillalai sun muku kwaf ɗaya,
Rami ne ku kuka gina.
Sun kama tudu sun tsallaka,
Sun bar ku a zafin rana.
Hajar ku idan sun sai da su,
Sun hau jirgi sai Ghana.
Ko Dubai, Indiya sun gano,
Sabon aure sun ɗana.
Ku ko cika baki ɗai ku ke:
“Ni ɗin nan ni ke suna.”
“Tarin makaranta zahiran,
Wallai ni ba mai fi na!”
“Ni ne Na-Filinge, ka dakata,
In ka yi musu zan tona.”
“Shago na je ka ga dandazo
Na masoya sun zo gu na.”
“Kullum a gida na har dubu,
Mata da maza mun gana.”
Wallahi ku farga abokanai,
Zancen nan nai mini ƙuna.
Ku ne fa ka haskaka duniya,
Littafi shi ku ka kunna.
Malammai, sha’ir, ƙirƙirau,
Amma a gane ku a raina?
Mai dokar barci, gyangyaɗi
Ya ɗaukai ya kai Chana?
Mafitar nan nema za ku yi,
To tilas sai kun zauna.
Domin tsoron ku aya ta ji,
To dutse sai kun tauna.
Kai tanƙwasa ƙarfe in gani,
Laushi nai tamkar waina.
Mudu kuka sawa tsaf a yau,
Garin ku ku bi shi ku auna.
Mota in an hau za a ja,
Injin ta fa sai an wana.
Zancen nan ni kam na gama,
Don Allah kadda ku raina.
Fata na lamiri na faɗa,
Kun ɗauka ni sai murna.
Nan zan ɗiga aya bissalam,
Wata rana in mun gana.
Baitin mu talatin sa biyar,
Na ƙirga ba in’ina.
Sunan mai baiti Iro ne,
Sa ‘Sheme’ gaban sa ka manna.
TAMAT
13 ga Satumba, 2012