• About
  • Contact
Sunday, June 29, 2025
  • Login
Ibrahim Sheme
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
No Result
View All Result
Ibrahim Sheme
No Result
View All Result
Home Da Hausa Waƙa

Goron Sallah

IBRAHIM SHEME by IBRAHIM SHEME
June 6, 2025
in Waƙa
0

Farkon ƙasida ba ni kai ku da nisa,
Sai nai salatin wanda bai da makusa,
Manzo mahaifin Fati Nana lawisa,
Sujada nake gun Wanda yai yo Isa,
Ya zame cikin hasken sa bawan Allah.

Jigon ta Sallah ce na wannan waƙe,
Murna muke ƙalbin mu ya ɗau haske,
Wannan biki lallai mu yi shi da gaske,
Ikhwan Musulmi ragunan mu a turke,
Layyar mu sai lagwada muna hamdala.

Sallah ta idi muka je mun yi ta,
Mun sa tufafi masu kyau domin ta,
Lada haɗa shiriya muna neman ta,
Liman yana huɗuba ƙwarai mun ji ta,
A zuwa da dawowa muna hailala.

Sunnar Ma’aiki ce fa sallar idi,
Domin cikar koyon sa Manzo Sidi,
Wannan da ya kawo shi Babban Kundi,
Ya zamo siraɗal mustaƙim, mun sirdi,
Mu tsaya a kai sam babu tsilla-tsilla.

In mun tsaya ƙyam babu inda-inda,
Bautar Ta’ala yin ta ba ma ganda,
Ladar tana da yawa garai shi wanda
Neman ta ya dage da kurɗa-kurɗa,
Balle a yau rana ta Babbar Sallah.

Ba a fushi kuma ba faɗa ba zagi,
Sai cin tuwo da miyar da ta sha magi,
Ko cin su shinkafa da kaji shirgi,
In kai yawan santi a sa maka waigi,
Soye na rago an cika maka kula.

Daga nan zumuncin ‘yan’uwan mu haƙiƙa,
Mota da mashin har su keke mu tuƙa,
Hatta da sawayen mu yanzu mu taka,
Da kiran waya ko tes mu zam mun miƙa
A farin ciki saƙon zumunci wallah.

Duka ‘yan’uwa na jini da sauran dangi,
Baban mu, Mama haɗa da tsagi-tsagi
Na aboka jumla babu sauran kingi,
A cikin su yau dai duk muna shawagi,
Mu je zumuncin nan na murnar Sallah.

Mai son ganin Sarki a gan shi a fada,
Don gaida zaki shugaba, don sada
Duka martaba domin cikar al’ada,
Kuma gun iyaye ka zamo ka jakada,
Riƙa yin hakan daidai a yau ba illa.

Haka ne ake yi duk a birnin Dabo,
Mu ma a KT mun jima mun sabo,
Birni na Shehu da yankuna har Yabo,
Sauran ƙasashen namu duk na ɗebo,
Daga can cikin Zazzau da birnin Yola.

Jama’a mu gode Zuljalal Rabbani,
Wannan da yai ƙwalwa ya ba ta tunani,
Da ya ba mu iko ƙauyuka har birni,
Ƙarfin zukata shi ya ƙara zabuni,
Komai muke yi mu yi domin Allah.

Allah Ta’ala ƙara ikon naka,
Sallar baɗin baɗaɗa mu gan ta da harka,
Ka zubo yawan haske a kowace garka,
Domin isar Manzo masoyin Makka,
Wato Muhammadu Ɗaha ɗan Abdallah.

Ni ma a nan zan dakata in nisa,
Kada in wuce marayi da bushin busa,
Har ma wanin ku ya ce da ni ya ƙosa,
Na shirya waƙar don mu sadu mu gaisa,
Rana ta yau don miƙa saƙon Sallah.

Tsarin bayani ga shi dalla-dalla,
Na kammala zancen mu filla-filla,
Allah ya yafen kuskuren da na ƙulla,
Wannan ƙasida wadda nai ran Sallah,
Baitin ta goma haɗa biyar kai jumla.

Burhama ni ne sha’irin da na yi ta,
E, Sheme ne sunan da zan ɗan gitta,
Na kwaɓa baitoci da fannonin ta,
Na yi su babu isa irin ta gwaninta,
A cikin muradi na na ɗokin Sallah.

Loading

Share this:

  • Facebook
  • X

Like this:

Like Loading...
Tags: BabbarSallahEidKabir
Previous Post

Wale Okediran @ 70: Tribute to a Workaholic Writer

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • Goron Sallah
  • Wale Okediran @ 70: Tribute to a Workaholic Writer
  • ‘Found in Translation: Writing in Indigenous Languages’
  • Motherland at 64
  • Cikar Shehu Ɗahiru Usman Bauchi shekara 100

Recent Comments

  1. UMAR IBRAHIM ABDULLAHI on Ta’aziyyar Hajiya Saratu Giɗaɗo (Daso) a Ranar Arba’in
Ibrahim Sheme No. 19, Chelsea Chibuzor Street, Katampe District Abuja, FCT Nigeria 📞 +234 0809 400 0071 (text) ✉️ ibrahimsheme@gmail.com
  • Home
  • About
  • Contact

© 2023 Ibrahim Sheme

No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings

© 2023 Ibrahim Sheme

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
%d