• About
  • Contact
Monday, June 30, 2025
  • Login
Ibrahim Sheme
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
No Result
View All Result
Ibrahim Sheme
No Result
View All Result
Home Da Hausa

Bikin ƙona littattafai a Kano

Ibrahim Sheme by Ibrahim Sheme
May 19, 2007
in Da Hausa
0
Cigaban Adabin Hausa: Ina Hausawan Ne?
Jami'an gwamnatin Kano tare da Sarkin Kano Ado Bayero su na cinna wa tarin littattafan Hausa wuta (Hoto: Ado Ahmad Gidan Dabino)

Jami'an gwamnatin Kano tare da Sarkin Kano Ado Bayero su na cinna wa tarin littattafan Hausa wuta (Hoto: Ado Ahmad Gidan Dabino)

Jami’an gwamnatin Kano tare da Sarkin Kano Ado Bayero su na cinna wa tarin littattafan Hausa wuta (Hoto: Ado Ahmad Gidan Dabino)

Kamar mako biyu da su ka gabata na je sayen jaridu a bakin Post Office na Kano, sai na ga babban labarin jaridar SUNDAY TRIUMPH ta ranar ya na cewa Gwamnatin Jihar Kano ta yi bikin ƙona littattafan Hausa a wata makarantar sakandare ta ‘yan mata. Na sayi jaridar saboda wannan labarin, a matsayi na na marubuci.

Hukumar A Daidaita Sahu ta Jihar Kano, wadda ke aikin tsaftace halayyar al’umma, ita ce ta shirya bikin ƙona littattafan. Kuma Gwamnan Kano da Sarkin Kano duk sun halarta.

Washegari, mun tattauna al’amarin da Dr Yusuf Adamu, wanda ya ce ya aika da saƙon rashin amincewa da wannan matakin ga shugaban A Daidaita Sahu ɗin, wato Malam Bala Muhammad. Daga bisani, mun kuma tattauna al’amarin da wasu marubutan, waɗanda su ka haɗa da Maje El-Hajeej Hotoro.

Ita hukumar ta ce ta ƙona littattafan ne saboda a ganin ta su na gurɓata tarbiyyar yara, musamman ‘yan makaranta, domin akwai batsa a cikin su. Kada a manta, hukumar ta taɓa shirya taron marubutan Hausa na zamani da ke Kano, a otal ɗin Tiga, aka yi musu jawabai kan al’amarin adabi. Tare da haɗin gwiwar Ƙungiyar Marubuta ta Nijeriya (ANA) reshen Jihar Kano, aka yi taron. An kuma biya marubutan ladar rubuta wasu ƙananan littattafai a bisa ruhin adabin da A Daidaita Sahu ta ke son a riƙa rubutawa. Tuni aka buga littattafan, aka raba su.

Shin ƙona littattafan ya dace? Me hakan zai haifar a nan gaba? Shin ya kamata marubuta su goyi bayan ƙona littattafai ko kuma su nuna rashin amincewa?

Loading

Share this:

  • Facebook
  • X

Like this:

Like Loading...
Tags: A Daidaita Sahuadabin Hausalittattafaimarubuta
Previous Post

Bikin kona littattafai – Amsar Abdalla

Next Post

My mission is to see people changing for the better, says Habu Dawaki

Next Post
Habu Dawaki

My mission is to see people changing for the better, says Habu Dawaki

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • Goron Sallah
  • Wale Okediran @ 70: Tribute to a Workaholic Writer
  • ‘Found in Translation: Writing in Indigenous Languages’
  • Motherland at 64
  • Cikar Shehu Ɗahiru Usman Bauchi shekara 100

Recent Comments

  1. UMAR IBRAHIM ABDULLAHI on Ta’aziyyar Hajiya Saratu Giɗaɗo (Daso) a Ranar Arba’in
Ibrahim Sheme No. 19, Chelsea Chibuzor Street, Katampe District Abuja, FCT Nigeria 📞 +234 0809 400 0071 (text) ✉️ ibrahimsheme@gmail.com
  • Home
  • About
  • Contact

© 2023 Ibrahim Sheme

No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings

© 2023 Ibrahim Sheme

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
 

Loading Comments...
 

    %d