• About
  • Contact
Tuesday, July 1, 2025
  • Login
Ibrahim Sheme
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
No Result
View All Result
Ibrahim Sheme
No Result
View All Result
Home Da Hausa

BUK Alumni: Karramawar har da ni!

IBRAHIM SHEME by IBRAHIM SHEME
February 28, 2008
in Da Hausa
0

A ranar Lahadi, 24 ga Fabrairu 2008 da safe ina ƙoƙarin barin Zaranda Hotel, a Bauchi, sai ga tes daga Dakta Yusuf Adamu mai ɗauke da kalma ɗaya rak, “Congrats.”

Na mayar masa da, “For what?” A rai na, ina jin wata tsokanar ce. To amma gaba na ya na faɗuwa: Ko an ba ni sadakar aure ne, ban sani ba?

Can sai ya maido da amsar cewa ban ga abin da aka buga a shafi na 7 na Sunday Trust ta ranar ba?

Na buga tes, na ce wallahi ban gani ba. Me su ka rubuta ne? Nan ma a rai na ina ta wasiwasi. Kai, ko an naɗa ni Ministan Harkokin Fetur ne?! (Wai ma!!!)

Gaba na ya na ta faɗuwa, ina jiran amsa. Can sai Yusuf ya maido da amsar cewa ai ina daga cikin mutanen da ALUMNI (ƙungiyar tsofaffin ɗaliban Jami’ar Bayero) za ta karrama a wurin gagarumin bikin saukar karatu da za a yi a mako mai zuwa. Malamin ya nanata cewa ina daga cikin MANYA irin su wane da wane da wane fa da za a karrama (har da tsofaffin gwamnoni).

To fa! To kuma ni me na yi da har za a karrama ni? Tambayar da na shiga yi wa kai na kenan lokacin da na bar otal ɗin, ni da aboki na, Badamasi Shu’aibu Burji (wanda ya raka ni birnin Bauchi don ganawa da Gwamna Malam Isa Yuguda, wanda mun gana da shi a daren ranar Asabar).

Mu ka shiga garin Bauchi, mu ka sayi jaridar Trust. A shafi na 7, mu ka ga sanarwa har shafi ɗaya. An lissafa jiga-jigan ƙasar nan da su ka taɓa yin BUK har mutum 50; ni ne na 15 a jerin: ”Alhaji Ibrahim Sheme, Editor, Leadership Newspaper.” To fa! Duk a jerin, babu yaro ko talaka kamar ni. Ana maka maganar jan wuya ne irin su:

– Alh. M.D. Yusufu (tsohon Sufeto Janar na ‘yan sanda)
– Col. Ɗangiwa Umar (tsohon Gwamnan Jihar Kaduna)
– Gwamnan Neja, Dakta Mu’azu Babangida
– Brig. Gen Yusuf Bomoi (shugaban hukumar NYSC ta ƙasa)
– Ambassador Usman Baraya (Ambasadan Nijeriya a Amurka na yanzu)
– Amb. Hassan Tukur (Fitaccen Jakada)
– Prof. Nuhu Yakub (VC, UniAbuja)
– Prof. Attahiru Jega (VC, BUK)
– Prof. Abdullahi Zuru
– Prof. Tijjani Bande (VC, UDU)
– Prof. Ruqayya Rufai (BUK)
– Senator Ahmed Sani Yarima (tsohon Gwamnan Zamfara)
– Hon. Farouk Lawan
– Haj. Aishatu Jibril Dukku (Ministar Ilimi)
– ds

Za a karrama mu a ranar 1 ga Maris, 2008 a Kano.

Har yanzun nan, idan na dubi gaggan manyan mutanen da ke cikin shafin jaridar nan, na kan yi tunanin: wace nasara na cimmawa a rayuwa da har na shiga ƙwaryar manya haka?

Babu shakka sai godiya ga Allah (SWT), mai kowa mai komai.

Shata ma ya faɗi:

“Ni ko yanzu kasuwa taw watse,
Ɗankoli da fura goran shi,
To shi ko kasuwa tai riba..”

Alhamdu lillah.

A KULA:
Shugaban Ƙungiyar Marubuta ta Nijeriya (ANA), reshen Abuja, Dr Emman Usman Shehu, shi ma ya na cikin jerin waɗanda za a karrama! Shi ne na 7 ma a jerin. Kai, mun gode Allah. Ni ban ma san BUK ya yi ba sai a ranar.

Loading

Share this:

  • Facebook
  • X

Like this:

Like Loading...
Tags: alumniBUKJami'ar Bayerokarramawa
Previous Post

Ashe Mace Ma Mutum Ce? Hira da Rahma Abdulmajid

Next Post

BUK Alumni Honours Leadership Editor

Next Post

BUK Alumni Honours Leadership Editor

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • Goron Sallah
  • Wale Okediran @ 70: Tribute to a Workaholic Writer
  • ‘Found in Translation: Writing in Indigenous Languages’
  • Motherland at 64
  • Cikar Shehu Ɗahiru Usman Bauchi shekara 100

Recent Comments

  1. UMAR IBRAHIM ABDULLAHI on Ta’aziyyar Hajiya Saratu Giɗaɗo (Daso) a Ranar Arba’in
Ibrahim Sheme No. 19, Chelsea Chibuzor Street, Katampe District Abuja, FCT Nigeria 📞 +234 0809 400 0071 (text) ✉️ ibrahimsheme@gmail.com
  • Home
  • About
  • Contact

© 2023 Ibrahim Sheme

No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings

© 2023 Ibrahim Sheme

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
%d