• About
  • Contact
Sunday, April 5, 2026
  • Login
Ibrahim Sheme
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
Ibrahim Sheme
No Result
View All Result
Ibrahim Sheme
No Result
View All Result
Home Da Hausa Waƙa

Ranar ‘Yar Gwagwarmaya

(Tukwici ga Zainab Ahmed 'bint Hijazi')

by IBRAHIM SHEME
April 06, 2022
0
Ranar ‘Yar Gwagwarmaya
Hajiya Zainab Ahmed

Hajiya Zainab Ahmed

0
SHARES
8
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Bismillah a farkon majlisi,

Ya Jallah biya ni buƙatu.

 

A gare ka na wo ƙoƙon barar

Fiƙira da yawa ta rubutu.

 

Yi salatin Khairul Anbiya,

Al-Khatam tsibiri na zukatu.

 

A cikin duka jerin manzuna,

Shi ne aka bai wa sarautu.

 

Mai yin koyi da Muhammadu,

Abadan tsira ya rabautu.

 

Ban ƙosawa a yabo nasa,

Jiddadun domin sa na bautu.

 

Baitika na riƙo kaya guda,

Na yabo a gurin Al-Bintu.

 

Ai yau kam ‘Birthday’ ɗin ta ce,

Murna ta saka na ƙagautu.

 

Al-Hijazi jikanyar Arab,

Da Fulani ingantattu.

 

Tsatso ta jinin Ɗanfodiyo,

Duk mai shakku, yi karatu.

 

Mowar Mama Ta-Gusau, ku ji,

Wato marubuciya Hafsatu.

 

Da Ahmadu gwarzo, malami,

Da ya koyar kar mu shagaltu.

 

Ya Rabbi jiƙai nasa da’iman,

Sanya shi cikin cetattu.

 

Shi da Mama haƙiƙan mun yaba,

Sun ba mu ɗiya da nagartu.

 

Mai kyan haiba mai kyan diri,

Fasalin ta ƙwarai ya saitu.

 

Zuciyar ta fara, launi fari,

Aikin ta a kai ta magantu.

 

Al-Hijazi da himma ta taho,

Don kawar mana duk gotattu.

 

Burin ta Arewa mu wattsake,

Mu zamo duka duk ‘yantattu.

 

A wajen tanyon jama’ar mu kaf,

Rayuwar ta a nan ta kwaɗaitu.

 

In ta na yaƙin ceton ƙasa,

Sai ka ɗauka ko ta zautu.

 

Ba ta shayin mai zare ido,

Janaral ne ko kuma kurtu.

 

Mai yin rawani ko zanzaro,

In dai ƙullin su mu cutu.

 

Ba ta tsoro, shakka ta cire,

Ai fahimtu ko a ɗimautu.

 

Ko a gan ta da rai, Hijazatu,

Ko ta kwanta can a matattu.

 

Ni fa shaida ne na gani da ji,

Ban dogara gun ɗan sautu.

 

Sam irin ta a mata ba yawa,

Kallabi a maza ta kaɗaitu.

 

Shi ya sa taragon su guda ɗaya,

Ita da Bintu Majid, Rahmatu.

 

In ka ce ba ka san Hijazi ba,

Tafi Facebook za ka wadatu.

 

Al-Muhaiminu kare Zainaba,

Haska ta cikin mu halittu.

 

Mai so ya ga bayan wagga ‘ya,

Latse shi ka bar shi a kuttu.

 

Domin darajar wannan wata,

Ramadana wata na karatu.

 

Mai waƙen nan aminin ta ne,

Ibrahimu mun daidaitu.

 

Nan ne kuma aya zan ɗiga,

Ba don gajiya ta rubutu.

 

Sai don kada zancen yai tsawo,

Har ku ce kun kasa karatu.

 

Baitin mu talatin da biyar,

Na tukwici gun Al-Bintu.

 

Ibrahim Sheme

Abuja

06/04/2022

Loading

Share this:

  • Click to share on Facebook (Opens in new window) Facebook
  • Click to share on X (Opens in new window) X

Like this:

Like Loading...
Tags: birthdayHafsatu Abdulwaheedtukwicizagayowar ranar haihuwaZainab Ahmed 'bint Hijazi'
Previous Post

Laifi ne idan an sayar da gidan Shata?

Next Post

Labari na: Tsakanin gimbiyar Zuru da ‘Yartsana

Next Post
Shafukan 'Yartsana

Labari na: Tsakanin gimbiyar Zuru da 'Yartsana

The late Adamu Yusuf

Remembering the late Adamu Yusuf (16th July, 1961 - 2nd August, 2007)

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • Tsokaci Kan Waƙar ‘Sarkin Bori Sule’ Ta Alhaji Mamman Shata Katsina
  • Bature Tanimu Gagare: Fighting, Not Just With His Pen
  • Goron Sallah
  • Wale Okediran at 70: Tribute to a Workaholic Writer
  • ‘Found in Translation: Writing in Indigenous Languages’

Recent Comments

  1. UMAR IBRAHIM ABDULLAHI on Ta’aziyyar Hajiya Saratu Giɗaɗo (Daso) a Ranar Arba’in
Ibrahim Sheme No. 19, Chelsea Chibuzor Street, Katampe District Abuja, FCT Nigeria 📞 +234 0809 400 0071 (text) ✉️ ibrahimsheme@gmail.com
  • Home
  • About
  • Contact

© 2023 Ibrahim Sheme

No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings

© 2023 Ibrahim Sheme

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
%d