SUNA: Tafiya Mabuɗin Ilmi: Balaguro A Isra’ila Da Palasɗinu
MARUBUCI: Ibrahim Sheme
KAMFANI: Informart Publishers, Kaduna
SHEKARA: 2005
SHAFUKA: 112
LABARIN: A cikin Disamba 1998, Mataimakin Editan jaridar New Nigerian Weekly, Malam Ibrahim Sheme, da wasu editocin jaridun Nijeriya, sun kai ziyara a ƙasar Isra’ila. A balaguron da suka yi, sun ziyarci wuraren tarihi a yankunan Isra’ila da Palasɗinu, kuma sun tattauna da manyan jami’an gwamnatin ta Yahudawa.
A wannan littafin, Malam Ibrahim ya ba da labarin tafiyar tasu a cikin lafazi mai daɗi da annashuwa, wanda a cikin sa ya riƙa yin hannunka-mai-sanda a kan dangantakar Musulmin duniya da Yahudu da Nasara, da batun ci-gaban ƙasashe, da tarihi, da kuma uwa-uba ƙalubalen da ke fuskantar wannan duniya tamu a cikin ƙarni na 21 miladiyya.
MARUBUCIN: Ibrahim Sheme ya taɓa riƙe manyan muƙamai a jaridu kamar su The Reporter, Nasiha, Rana, Hotline, da New Nigerian. Ya samu digirin sa na farko a Jami’ar Bayero, Kano, a cikin 1989, sa’annan a cikin 1994 ya samo digiri na biyu a Jami’ar Wales da ke birnin Cardiff a ƙasar Birtaniya, inda ya karanci aikin jarida. Shi ne mawallafin mujallun Fim, Bidiyo, da Bahaushiya, uku daga cikin fitattun mujallun Hausa na wannan zamanin. An wallafa littatafan da na ƙagaggun labarai da dama, waɗanda suka haɗa da Kifin Rijiya, wanda ya zo na biyu a Gasar Rubuta Ƙagaggun Labarai Cikin Harsunan Mu Na Gado wadda aka yi a cikin 1989, da The Malam’s Potion, da kuma ‘Yartsana. An taɓa buga Ilmi Mabuɗin Tafiya da Turanci a cikin New Nigerian Weekly da kuma mujallar Fim. A yanzu, Ibrahim Sheme ne Editan jaridar Leadership da ke Abuja.
![]()


