• About
  • Contact
Sunday, July 27, 2025
  • Login
Ibrahim Sheme
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
No Result
View All Result
Ibrahim Sheme
No Result
View All Result
Home Da Hausa

Sashen Hausa na rediyon Faransa

IBRAHIM SHEME by IBRAHIM SHEME
May 12, 2007
in Da Hausa
0

Mahamane Salisu Elh Hamissou, dan jarida mazaunin birnin Yamai na kasar Nijar, ya ba mu labarin cewa a ranar Talata mai zuwa, 15 ga Mayu 2007, da misalin karfe 7: 30 agogon Nijeria da Nijar (bai fadi ba ko na dare ko na safe) sashen Hausa na rediyon kasar Faransa (Radio France International) zai fara watso shirye-shiryen sa kai-tsaye daga birnin Ikko na tarayyar Nijeria. Shi Salisu ya na daya daga cikin ma’aikatan da aka dauka su yi aiki a wannan sabon sashe.

A gaskiya na yi murnar jin wannan albishir da aka yi mana. A gani na, bude sashen Hausa a RFI ya k’ara nuna mana muhimmancin wannan harshe a fagen watsa labarai a duniya. Alhamdu lillahi. Allah ya ba su sa’a amin.

To amma ina da tambayoyi:

1. Salisu ya ce karfe 7:30 ne za a fara shirin, amma bai ce na SAFE ba ne
ko na DARE.
2. Bai fad’i a wace mita da kuma wane zango (wato SW ko MW ko FM)
za a kama rediyon ba.

Ina ba da shawara ga shugabannin gidan rediyon da su saka
talla a kafafen watsa labarai da ke akwai don su sanar da jama’a
labarin kafa wannan sashe na Hausa. Ina nufin kafafe na Hausa kamar
Gaskiya Ta Fi Kwabo, Aminiya, Leadership Hausa, Rediyon Nijeriya
Kaduna, Nagarta Radio, Freedom Radio, da sauran su.

Bayan haka, yaya na ji wai a Legas su ke, maimakon Paris? Wani sabon
salo ne? Anya ba su gudun kada wata rana jami’an tsaron Nijeriya su
kai musu ziyara idan su ka watsa wani labari da jami’an ba su so? Ka san fa daya daga cikin dalilan ‘yancin da BBC Hausa da VOA Hausa su ka samu shi ne saboda sun yi wa jami’an Nijeriya nisa! Hattara!

Loading

Share this:

  • Facebook
  • X

Like this:

Like Loading...
Previous Post

At home with Labo Yari

Next Post

Mun zama shugabanni a shirin fim

Next Post

Mun zama shugabanni a shirin fim

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • Bature Tanimu Gagare: Fighting, Not Just With His Pen
  • Goron Sallah
  • Wale Okediran @ 70: Tribute to a Workaholic Writer
  • ‘Found in Translation: Writing in Indigenous Languages’
  • Motherland at 64

Recent Comments

  1. UMAR IBRAHIM ABDULLAHI on Ta’aziyyar Hajiya Saratu Giɗaɗo (Daso) a Ranar Arba’in
Ibrahim Sheme No. 19, Chelsea Chibuzor Street, Katampe District Abuja, FCT Nigeria 📞 +234 0809 400 0071 (text) ✉️ ibrahimsheme@gmail.com
  • Home
  • About
  • Contact

© 2023 Ibrahim Sheme

No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings

© 2023 Ibrahim Sheme

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
%d