• About
  • Contact
Sunday, July 27, 2025
  • Login
Ibrahim Sheme
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
No Result
View All Result
Ibrahim Sheme
No Result
View All Result
Home Da Hausa

MACE MUTUM!

IBRAHIM SHEME by IBRAHIM SHEME
January 2, 2008
in Da Hausa
0
MACE MUTUM!
Mace

A yau Alhamis (ko in ce jiya, tunda karfe 1 ta haura) na shiga kasuwar Wuse, Abuja, inda na samu sayen littafin Mace Mutum na Rahma A. Majid. N820 na saye shi. Littafin ya ɗan yi kwana biyu da fitowa ban gan shi ba, ga shi kuwa wai ni ma ɗan gida ne (tunda “ƙanen” marubuciyar ne!). Hasali ma dai na aika wa da wasu littafin, ciki har da Amina Abdulmalik (mai ‘Ruwan Raina’), wadda ta na Katsina yanzu, na sa Ɗanjuma Katsina ya kai mata kwafe har gida, kuma ta karanta har ta gama cikin ƙanƙanen lokaci!

Na aje littafin a kan teburi na a ofis. Duk wanda ya shigo sai ya ɗauka, ya yi mamakin girman sa, har wasu na cewa, “Wannan tarihin waye?” Ba su ga hoton Yar’Adua ko Babangida a bangon ba! Sai na ke ce musu, “Ai novel ne.”

“Novel? Da ma ana yin novel da Hausa haka?”

Mutane sun saba da ganin littafi mai shafi 40 zuwa 70 na Hausa. Shi ‘Mace’Mutum’, shafi 520 ne. Wane yaro?!

Kai, lallai Rahma ta ciri tuta! Mace mai kamar maza, kwari ne babu! Matar soja kin fi ƙarfin yaro!

Allah ya sa sauran marubuta za su ɗauki hannu, su yi koyi da ita. Ni da ma na shafe shekaru ina yekuwar cewa ya kamata marubutan mu su riƙa yin rubutu mai inganci, kuma su riƙa yin littafi mai kauri-kauri. Su yi ƙoƙarin ficewa daga ƙangin ‘Adabin Kasuwar Kano.’ To, Rahma dai ta fara. Allah ya ƙara mata basira, da ƙwarin gwiwa.

Gobe (ko kuwa dai a yau!) zan fara karanta shi in-sha Allahu.

Kuma na ƙudiri aniyar saya wa marubuciya Sa’adatu Baba Ahmad Fagge kwafe ɗaya in kai mata a gidan su a nan Abuja (domin fa ta na gari yau mako biyu, kuma na ziyarce ta sau biyu, gobe ma zan koma). Zan ba ta mamaki da kyautar littafin, domin ita ma har yanzu labarin sa kawai ta ke ji. Za mu yi tseren gama shi kenan.

Sallaman ku!

Loading

Share this:

  • Facebook
  • X

Like this:

Like Loading...
Previous Post

I Publish Tozali To Promote Northerners – Maimuna

Next Post

Shu’aibu Makarfi – Grandfather of Hausa Drama

Next Post
Shu'aibu Makarfi

Shu'aibu Makarfi - Grandfather of Hausa Drama

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • Bature Tanimu Gagare: Fighting, Not Just With His Pen
  • Goron Sallah
  • Wale Okediran @ 70: Tribute to a Workaholic Writer
  • ‘Found in Translation: Writing in Indigenous Languages’
  • Motherland at 64

Recent Comments

  1. UMAR IBRAHIM ABDULLAHI on Ta’aziyyar Hajiya Saratu Giɗaɗo (Daso) a Ranar Arba’in
Ibrahim Sheme No. 19, Chelsea Chibuzor Street, Katampe District Abuja, FCT Nigeria 📞 +234 0809 400 0071 (text) ✉️ ibrahimsheme@gmail.com
  • Home
  • About
  • Contact

© 2023 Ibrahim Sheme

No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings

© 2023 Ibrahim Sheme

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
%d