• About
  • Contact
Sunday, April 5, 2026
  • Login
Ibrahim Sheme
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
Ibrahim Sheme
No Result
View All Result
Ibrahim Sheme
No Result
View All Result
Home Da Hausa

Maryam Usman Hiyana ta haihu

by IBRAHIM SHEME
August 04, 2008
0
0
SHARES
20
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Mata ku zo ku yi gud’a: “Ayyiririii!!”

Shahararriyar jarumar nan ta finafinan Hausa, Maryam Usman (Hiyana), ta haihu. Wata majiya ta sanar da ni cewa a ranar Lahadi da ta wuce ne Maryam din ta haihu. An samu d’a namiji.

A cewar majiyar, Maryam ta haihu ne a birnin Kano, a wani asibiti mai zaman kan sa.

Idan kun tuna, Maryam ta shiga tsaka-mai-wuya sakamakon bullar majigin batsa da su ka dauka ita da wani saurayin ta mai suna Bobo. Majigin, wanda aka dauka da wayar hannu, ya bulla ne a farkon watan Agusta 2007. Nan da nan ya fantsama a cikin al’umma kamar wutar bazara.

Bullar majigin ya sa jarumar ta shiga buya, ta bar industiri ana ta cece-ku-ce; kai, ba ma industiri ba, har da dukkan kasar Hausa da sauran sassa na duniya.

Bayan watanni uku ana cacar baki, a cikin Nuwamba 2007 sai wani namijin duniya, wanda ya dade ya na soyayya da Maryam, ya aure ta. Wannan ba wani ba ne illa Alhaji Ado Ahmed Dangulla, wani dan kasuwa a Kano. Auren da su ka yi ya burge mutane da dama, musamman masoyan Hiyana. An yi masu fatan alheri.

To amma hayaniyar Hiyana-Bobo din nan ta yi wa sana’ar fim babbar illa. Gwamnatin Jihar Kano ta jefo da wani mutum mai suna Malam Rabo cikin lamarin, a matsayin shugaban Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano. Ba tare da bata lokaci ba, malamin ya k’ara ingiza harkar fim cikin mawuyacin hali: ya dakatar da sana’ar fim har wata shida, daga bisani kuma ya kulle manyan ‘yan wasa, da furodusoshi da ‘yan kasuwar finafinai, ban da kamfen din batanci kan ‘yan fim da ya shiga yi a kafafen watsa labarai. A yanzu haka akwai shari’u da ake tafkawa da shi a kotu.

Ko ma dai yaya ta je ta dawo, ita Hiyana ta yi zaman ta lafiya lau da mijin ta. Na ji an ce rayuwar auren su abar burgewa ce. To amma tuni ta yi bankwana da shirin fim. Hasali ma dai, ba ta yarda ta yi mu’amala da ‘yan fim, sai ‘yan kalilan (irin su Maryam Oloni).

A cewar majiya ta, Hiyana da d’an da ta haifa su na nan cikin k’oshin lafiya. Ranar Lahadi za a yi suna. (Wasu sun ce sunan mahaifin ta, wato Usman, za a rad’a wa yaron).

To ko ma dai me aka rada masa, mu tamu ita ce addu’ar Alah Ya raya shi cikin k’oshin lafiya. Kuma Allah Ya ba uwa lafiyar mama, amin.

Loading

Share this:

  • Click to share on Facebook (Opens in new window) Facebook
  • Click to share on X (Opens in new window) X

Like this:

Like Loading...
Previous Post

Hausa Actress, Maryam Hiyana, Puts To Bed

Next Post

Hiyana: An Yi Suna, An Samu ‘Daddy’!

Next Post

Hiyana: An Yi Suna, An Samu 'Daddy'!

KOTU TA SOKE BELIN IYAN-TAMA

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • Tsokaci Kan Waƙar ‘Sarkin Bori Sule’ Ta Alhaji Mamman Shata Katsina
  • Bature Tanimu Gagare: Fighting, Not Just With His Pen
  • Goron Sallah
  • Wale Okediran at 70: Tribute to a Workaholic Writer
  • ‘Found in Translation: Writing in Indigenous Languages’

Recent Comments

  1. UMAR IBRAHIM ABDULLAHI on Ta’aziyyar Hajiya Saratu Giɗaɗo (Daso) a Ranar Arba’in
Ibrahim Sheme No. 19, Chelsea Chibuzor Street, Katampe District Abuja, FCT Nigeria 📞 +234 0809 400 0071 (text) ✉️ ibrahimsheme@gmail.com
  • Home
  • About
  • Contact

© 2023 Ibrahim Sheme

No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings

© 2023 Ibrahim Sheme

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
%d