• About
  • Contact
Sunday, July 27, 2025
  • Login
Ibrahim Sheme
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
No Result
View All Result
Ibrahim Sheme
No Result
View All Result
Home Da Hausa

An Kulle Bashir Ɗandago A Jarun

IBRAHIM SHEME by IBRAHIM SHEME
August 6, 2009
in Da Hausa
0
An Kulle Bashir Ɗandago A Jarun
Malam Bashir Ɗandago

Shugaban Hukumar Hukunta ‘Yan Fim ta Jihar Kano, Malam Abubakar Rabo, ya cika alƙawarin sa na cewa sai ya ɗaure ɗaya daga cikin fitattun mawaƙan Kano, wato Malam Bashir Ɗandago. Domin kuwa a yau dai jami’an hukumar sun kama shi, sun gurfanar da shi a gaban kotun hukunta ‘yan fim.

Haka kuma an kama wani matashi mai suna Kabir Maulana.

Laifin da ake tuhumar su da shi, shi ne: wai sun saki faifan waƙar ‘Tsangayar Kura’ (mai ɗauke da waƙar nan ta “Hasbunallahu” ) bayan hukuma ta hana sakin faifan a Kano.

A kotu, su Ɗandago sun ce, “Not guilty.” To amma Alƙali Mukhtar Ahmed, kamar yadda ya saba yi, ya hana belin su, ya tura su gidan yari. Ya ce a dawo ran Litinin a ci gaba da magana. Manufa ita ce, su ma dai sun yi zaman jarun.

Ga waɗanda su ka saurari waƙar “Hasbunallahu, ” za su tuna da cewa akwai muryar Malam Bashir Ɗandago a ciki. To, da ma kaska ta na da haushin kifi.

Shi dai Ɗandago, ya yi fice ne a fagen waƙoƙin yabon Manzon Allah (SAW), wato waƙoƙin bege. A cikin 2009 ne aka ji muryar sa a waƙar “Hasbunallahu, ” wanda hakan ya ƙara wa waƙar ƙarfi da karsashi. A wata hira da ya yi da ‘yan jarida kwanan baya, Ɗandago ya ce ya yi waƙar ne domin ya taimaka wajen murƙushe zaluncin da ake yi a Kano.

Kwanan nan kotun ta su “Asabe Murtala” ta ɗaure jagaban waƙar “Hasbunallahu, ” wato Malam Aminuddeen Ladan Abubakar (ALA), a gidan yari. Za a ci gaba da shari’ar sa a makon gobe.

Majiya ta ce gurfanar da Rabo da ‘yan fim su ka yi a ofishin ‘yan sanda na Metro kwanan nan ya ƙara hayaƙa malamin, har ya sha alwashin yin ramuwa.

Majiyar ta ce don haka dai kwanan nan hukumar za ta kama wasu mata daga cikin ‘yan fim, musamman mawaƙan da ke cikin su. Sannan majiyar ta ce ana nan ana haƙon wani ɗan fim, tare da shan alwashin cewa a gidan yari zai yi azumin Ramadan.

“Zalunci ba zai ɗore ba” – Maryam A. Baba, a waƙar “Rabo, Rabo”

Loading

Share this:

  • Facebook
  • X

Like this:

Like Loading...
Previous Post

Police Arrest Kano Censors Board DG

Next Post

Vision of the Jewel

Next Post
Vision of the Jewel

Vision of the Jewel

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • Bature Tanimu Gagare: Fighting, Not Just With His Pen
  • Goron Sallah
  • Wale Okediran @ 70: Tribute to a Workaholic Writer
  • ‘Found in Translation: Writing in Indigenous Languages’
  • Motherland at 64

Recent Comments

  1. UMAR IBRAHIM ABDULLAHI on Ta’aziyyar Hajiya Saratu Giɗaɗo (Daso) a Ranar Arba’in
Ibrahim Sheme No. 19, Chelsea Chibuzor Street, Katampe District Abuja, FCT Nigeria 📞 +234 0809 400 0071 (text) ✉️ ibrahimsheme@gmail.com
  • Home
  • About
  • Contact

© 2023 Ibrahim Sheme

No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings

© 2023 Ibrahim Sheme

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
%d