• About
  • Contact
Sunday, April 5, 2026
  • Login
Ibrahim Sheme
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
Ibrahim Sheme
No Result
View All Result
Ibrahim Sheme
No Result
View All Result
Home Da Hausa

Taƙaitaccen Tarihin Alhaji Hassan Wayam Maikukuma

by IBRAHIM SHEME
September 08, 2019
0
Alhaji Hassan Wayam Maikukuma
Alhaji Hassan Wayam Maikukuma

Alhaji Hassan Wayam Maikukuma

0
SHARES
22
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

An haifi Alhaji Hassan Wayam a wani gari mai suna Gwadda, wanda kuma ake kira Bakin Ruba, a ƙasar Maradun ta Jihar Zamfara, a cikin 1956.

Mahaifin sa, Mal. Muhammadu, Babarbare ne. Mahaifiyar sa, Halima, Bafulatana ce. Sana’ar mahaifin ita ce sassaƙa, amma wani lokaci ya kan yi wa Fulani kiɗan kotso jefi-jefi.

Ya na yaro ƙarami, sai mahaifin sa ya koma wani gari mai suna Ƙunci da zama, can gabas da birnin Gusau. 

Da Hassan ya ɗan data, sai ya koma Mayanci, nan kusa da Gusau, ya zama yaron kanikawa. To Mayanci bariki ce sosai a lokacin, ga karuwai da ‘yan caca da sauran ‘yan duniya. A nan sha’awar sa da kaɗe-kaɗe ta yi zurfi, musamman kiɗan kukuma. Amma bai fara koyo ba sai da ya koma gida Ƙunci. A can ya fara ɗinka kukuma da hannun sa. A duk lokacin da ya samu lokaci ya kan goga abar sa da hannun sa, amma a ɓoye.

Da ya ƙara wayo, sai ya sake komawa Mayanci, ya zama yaron wata mata, ya na wasa a gidan ta. To sojoji na yawan wucewa ta Mayanci, kuma su kan yada zango a can su ci abinci ko ma su kwana. Ta haka ne ya haɗu da wani soja mai suna Ali Barau, wanda ya buƙaci matar nan ta ba shi Hassan ya tafi da shi Zariya. Ta ce, “To ga shi nan amana.”

Alhaji Hassan Wayam

Ali Barau ya kai Wayam Zariya a cikin 1969, ya aje shi a gidan sa da ke Unguwar Kanawa. Duk yamma sai ya ɗauke shi ya kai shi barikin soja, ya riƙa yi wa sojoji wasa.

Dalilin zuwan shi Zariya kenan.

(Wannan tsakure ne daga wata hira da na sa wani wakili na, Usman Modibbo, ya yi mani da Hassan Wayam a cikin shekarar 1992, lokacin ina Editan mujallar Rana ta kamfanin Hotline, Kaduna. An buga hirar a cikin mujallar ta ranar 19 ga Oktoba, 1992, shafi na 17 da na 18. Modibbo ya yi Kwamishinan Ilimi na Jihar Kaduna, kuma yanzu farfesa ne.)

An ɗauki waɗannan hotunan na Alh. Hassan Wayam shekaranjiya a wajen bikin Dakta Ilham, ɗiyar Ɗanmalikin Kano, Amb. Ahmed Umar, a Kano. Allah ya ƙara masa lafiya da nisan kwana, amin.

Loading

Share this:

  • Click to share on Facebook (Opens in new window) Facebook
  • Click to share on X (Opens in new window) X

Like this:

Like Loading...
Previous Post

The Life of Bature Gagare (1958-2002), Author of the Novel ‘Ƙarshen Alewa Ƙasa’

Next Post

Sabuwar Dokar Cire Ko Saka Kuɗi A Banki

Next Post
Sabuwar Dokar Cire Ko Saka Kuɗi A Banki

Sabuwar Dokar Cire Ko Saka Kuɗi A Banki

Kyaftin Adamu Suwa Ɗanbaba

'Saja-Manja Adamun Panshin' - Shekara 50 Bayan Rasuwar Kyaftin Ɗanbaba

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • Tsokaci Kan Waƙar ‘Sarkin Bori Sule’ Ta Alhaji Mamman Shata Katsina
  • Bature Tanimu Gagare: Fighting, Not Just With His Pen
  • Goron Sallah
  • Wale Okediran at 70: Tribute to a Workaholic Writer
  • ‘Found in Translation: Writing in Indigenous Languages’

Recent Comments

  1. UMAR IBRAHIM ABDULLAHI on Ta’aziyyar Hajiya Saratu Giɗaɗo (Daso) a Ranar Arba’in
Ibrahim Sheme No. 19, Chelsea Chibuzor Street, Katampe District Abuja, FCT Nigeria 📞 +234 0809 400 0071 (text) ✉️ ibrahimsheme@gmail.com
  • Home
  • About
  • Contact

© 2023 Ibrahim Sheme

No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings

© 2023 Ibrahim Sheme

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
 

Loading Comments...
 

    %d