• About
  • Contact
Sunday, April 5, 2026
  • Login
Ibrahim Sheme
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
Ibrahim Sheme
No Result
View All Result
Ibrahim Sheme
No Result
View All Result
Home Columns Online Musings

Waƙar ‘Baƙar Rama’ ta Haruna Uji

by IBRAHIM SHEME
July 24, 2018
0
Waƙar ‘Baƙar Rama’ ta Haruna Uji
0
SHARES
4
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

 

Haruna Uji ya na kaɗa gurmin sa

Na rubuta wannan waƙar daga wani faifai na Alhaji Haruna Uji a ranar 21 ga Mayu, 2015. A lura da cewar da yake Uji ya rera wannan waƙar a lokuta daban-daban, mai yiwuwa ne ka ji wani samfur na waƙar wanda ya bambanta da wannan da na rubuto.

Waƙar “Baƙar Rama” dai Haruna Uji ya yi wa matar sa Tasalla ne, don nuna shauƙin soyayya da ke tsakanin su. Bismilla:

*

 Ruwa isa gayya, Baƙar Rama,
Ruwa isa gayya, ya ki!
Allah Sarki, Baƙar Rama,
Ke ‘yar masara mai yawan zani,
Sannu da rana, Tasalla!

Na kaɗa gangar Baƙar Rama
Wa’yansu mutane su na faɗi: “Baƙar Rama ko ba mutum ba ce?!”
Na ce musu, “A’a, ku bar faɗi, Bakar Rama amma mutum ta ke.”

Ai sai su ka ce min: “Haru Uji, Baƙar Rama in dai mutum ta ke,
Ka yi mana taɗin Baƙar Rama.”
Sai na ce “Na yarda!”

Sai ku matso zan gaya muku,
Na farko zancen Baƙar Rama,
Mai son ‘yar nan Baƙar Rama,
In gan shi ga kogo kamar guza kamar gansheƙa, ya ja ciki,
Ta ce ba ta so, ba za ta ba.

Ina mai son ki?
In kai shi ga kogi,
Iy yi nutso ya ɗebo yashi,
Sai ya ƙirge yashi,
Baƙar Rama ta ce ba ta so, ba za ta ba!

In ya haɗa wannan,
In kai shi ga rairai ya tandara,
Ta ce ba ta so!
Ya hau kan rimi,
Sai ya kere rimi, ya faɗi da ƙirji,
Baƙar Rama ta ce ba ta so, ba za ta ba!

Mai son ‘yar nan Baƙar Rama,
Ya zabura sosai,
Ya je dawa ya samu giginya,
Ya hau giginya da baya,
Baƙar Rama ta ce ba ta so!

In ya haɗa wannan,
Ya zauna ya yi mata kukan wata bakwai da kwana hamsin,
Sai ta ce ba ta so, ba za ta ba.

Allah Sarki, Baƙar Rama!

Loading

Share this:

  • Click to share on Facebook (Opens in new window) Facebook
  • Click to share on X (Opens in new window) X

Like this:

Like Loading...
Previous Post

Waƙar ‘Baƙar Rama’ ta Haruna Uji

Next Post

Garba Dangida at 62: A Short Appreciation

Next Post
Alhaji Garba A. Dangida in his office - in those days!

Garba Dangida at 62: A Short Appreciation

Waƙar “Taimaka Rabbana” ta Sani Sabulu Kanoma

Waƙar "Taimaka Rabbana" ta Sani Sabulu Kanoma

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • Tsokaci Kan Waƙar ‘Sarkin Bori Sule’ Ta Alhaji Mamman Shata Katsina
  • Bature Tanimu Gagare: Fighting, Not Just With His Pen
  • Goron Sallah
  • Wale Okediran at 70: Tribute to a Workaholic Writer
  • ‘Found in Translation: Writing in Indigenous Languages’

Recent Comments

  1. UMAR IBRAHIM ABDULLAHI on Ta’aziyyar Hajiya Saratu Giɗaɗo (Daso) a Ranar Arba’in
Ibrahim Sheme No. 19, Chelsea Chibuzor Street, Katampe District Abuja, FCT Nigeria 📞 +234 0809 400 0071 (text) ✉️ ibrahimsheme@gmail.com
  • Home
  • About
  • Contact

© 2023 Ibrahim Sheme

No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings

© 2023 Ibrahim Sheme

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
 

Loading Comments...
 

    %d