• About
  • Contact
Sunday, April 5, 2026
  • Login
Ibrahim Sheme
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings
Ibrahim Sheme
No Result
View All Result
Ibrahim Sheme
No Result
View All Result
Home Da Hausa Waƙa

Wasu baitocin marigayi Malam Lawan Maiturare

by MALAM LAWAN MAITURARE
September 05, 2018
0
0
SHARES
8
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Ƙaunar Muhammadu na nutse ba waiwaye,
Na sanya kai na can ciki na dulmiya,
Ya hamidan Mahmudu ban da kamar ka.

Ya Annabin rahama gare ka na durƙusa,
Al-Musɗafa kai ne ka san matuƙar isa,
Mai son ka ma ya san isa domin ka.

Kaicon mutum ya san ka in bai so ka ba,
Kaicon mutum bai so ka don bai san ka ba,
Ba arziƙi gun wanda ba ya son ka.

Tsuguno da zaunawa da miƙewa tsaye,
Tafiya da hango nesa har mu yi waiwaye,
Mun sami wannan arziƙi domin ka.

Ya Ɗahirun mai kyan jiki da na zuciya,
Muɗahhiran ka tsarkake mana ƙungiya,
Hadi ka na shiryar da mai ƙaunar ka.

Al-Musɗafa kai ne iya matuƙar rabo,
Mai son ka sai mai arziƙi kuma mai rabo,
Ba arziƙi faufau wajen maƙiyan ka.

Mutari du mai son ka ya gama arziƙi,
Mahmudu wanda ya ƙi ka ya rasa arziƙi,
Domin ko ba wani arziƙi sai naka.

Mutari jikan Nuhu in ba don ka ba,
Wallahi du taron mu da ba a yi mu ba,
Mun shaƙi ƙamshin arzikin nan naka.

Ya mai siraɗal mustaƙima mamallaki,
Don Murtala Hadi rasulun arziƙi,
Al- Musɗafa jirgin fiton bayin Ka.

Ya Rabbu mai Malakutu mai ma’ul haya,
Don sahibin Jibrila gwarzon Mariya,
Hasken ibada maganin mai shirka.

Mun roƙi alfarma saboda abin biya,
Mun tuba mun kora da ƙaunar zuciya,
Mun durƙusa Allah mu na roƙon Ka.

Ba za mu sami abin da bai zama naka ba,
Wa za mu ce wa ya ba mu in ba Ka ba mu ba?
Ka san buƙata ce da mu bayin Ka.

Ka ce a sa bakin da bai saɓe Ka ba,
Ban wo gaban kai na wajen roƙon Ka ba,
Shi ne na zo gun Musɗafa manzon Ka.

* Daga MALAM LAWAN MAITURARE (1976)

Loading

Share this:

  • Click to share on Facebook (Opens in new window) Facebook
  • Click to share on X (Opens in new window) X

Like this:

Like Loading...
Tags: Malam Lawan Maiturare
Previous Post

Adam A. Zango a bangon mujallar Fim

Next Post

Yadda Na Jagoranci Rubuta Littafin Tarihin Mamman Shata

Next Post
Littafin "Shata Ikon Allah!"

Yadda Na Jagoranci Rubuta Littafin Tarihin Mamman Shata

Karairayi 16 A Martanin Aliyu Ibrahim Kankara

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recent Posts

  • Tsokaci Kan Waƙar ‘Sarkin Bori Sule’ Ta Alhaji Mamman Shata Katsina
  • Bature Tanimu Gagare: Fighting, Not Just With His Pen
  • Goron Sallah
  • Wale Okediran at 70: Tribute to a Workaholic Writer
  • ‘Found in Translation: Writing in Indigenous Languages’

Recent Comments

  1. UMAR IBRAHIM ABDULLAHI on Ta’aziyyar Hajiya Saratu Giɗaɗo (Daso) a Ranar Arba’in
Ibrahim Sheme No. 19, Chelsea Chibuzor Street, Katampe District Abuja, FCT Nigeria 📞 +234 0809 400 0071 (text) ✉️ ibrahimsheme@gmail.com
  • Home
  • About
  • Contact

© 2023 Ibrahim Sheme

No Result
View All Result
  • Home
  • Bookworm
  • Book Publishing
  • Media
    • News & Events
    • Gallery
  • Blog
    • Columns
      • Blueprint
      • Leadership Weekend
    • Da Hausa
    • Online Musings

© 2023 Ibrahim Sheme

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
%d