Taken Shago Wanda Makaɗa Bawa Ɗan’anace Gandi Ya Yi Masa

Wannan waƙa na ɗaya daga cikin waƙoƙin Ɗan’anace waɗanda su ka sa na haƙƙaƙe da cewa har ƙasa ta naɗe babu makaɗin dambe irin shi. Ko ita kaɗai ya rera, ta isa ta ɗar ma sa’a! Saboda ita kaɗai, ni idan mutum ya ce akwai makaɗin dambe da ya zarce Ɗan’anace sai in ji kamar zagi na ya ke yi!

Ga waƙar na yi karambanin rubutawa. Amma na haɗe kalaman jagoran da na ‘yan amshin domin kusan tare su ke tafiya a waƙar sau da yawa. A taimaka da gyara inda na yi kuskure:

Taho Na-Bakura ɗan Abdu gazaguru.
To bahago,
Ina mazan da ka i ma?
 

Ɓaleri sannu mai hana ƙarya!

Ka nai da wa ka nai da aboki,

Kuma ka nai da ɗa ka nai da uba nai.

Ɗan Audu gazaguru,
Kai ji duna ya tare hanyab Bakura ya tare Mafara,
Ɗan Audu ya tare Rini,
Kowaz  zo Kufoji ya ishe bayi wa’anda ba a wa takakka,
Wandara kai dai ka wa mutum takakka,

In ka zo ka ko buge shi ka dawo!

In ka zo ka ko buge su ka dawo!

Arne ka biya na Mande na sarkin ɗiya,
Tafo na Kallamu Musa,
Ina arne mai halin Hasau na Maraɗi?

Shago irin kiɗin ga da ni ma duk da Hasau ga su Ɗanwaire ba a yi ma haka nan ba.

Ɗa ya tuna da lahira ya ka kwana,

Bale zuwa gidan alƙali.

Gabas da yamma, dama da hauni, kudu da arewa,
Wandara ka dai hana ma runji suna,
Yanzu mutum ko ya yi dambe ba shi da suna,
In dai ina buga kawo.
Bari mu hwaɗa masu runjin ga masu tsafin dambe saboda bawan Sarki:
Maza ka cin ƙurungun kura,
Wandara sai jan karen da yay yi zagogi.
Duna ga wanga zamani ba wani ba,
Mutum ko ya kashe ka ba shi da suna,
In kau ka kashe su ka yi gaba ɗai.
To ko an kashe ka ban jin komi,
Ɓarnad da ka yi shi su ka ranko!
Yaƙi ya ci annabawa Shago,

Bale Ɓaleri mai naɗe hannu.

Yaƙi ya kashe talaka da barde,

Daɗa fa ga kare ga kura ɗan Abdu gazaguru,
Ga kare ga kura,
Wandara mi ka kai da rai ga arna?
Gama na san halin maso rai wawa.
Duna, maso rai wawa,
Tafi a kashe ka gaba ɗai na Ɗan’anace Shagon Mafara,

Na zaune bai ga gari ba.

‘Yan maza kun ji kiɗin kututturu na Bakura,
Duna mahaukaci na yamma ga Rini,
Rigima’ aradu mai ɗime kurma,
Mutuwa ina ruwan ki da tsoho?
Kai shi lafira gidan Ɗangangu!
Gurunzumi abin zuba shara,
Samji irin hakin da ka ramno,
Lafira a kai maki gawa!
Yaro gafarak ka ga sababi nan,
Kada aradu ta far ma,
Halan ba ka san halin ƙanen ajali ba,
Sannu da ɗibash sheɗa,
Mutuwa ke daɗe ki na kashe bayi.

Kai! Kai! To!

In da lahira ana aza dambe,

Da Wanakiri ya ji ƙwal ga gaba nai!

Ɗan Audu bawan Sarki,
Sannu baƙin mutum baran Sardauna,
Wandara ka riƙa ma Antaru fama,
Na-Kande tuji mai shan ruwa kwatarmin kura,
Goga ko kai dare ka nai mani rana,
Ɗan Abdu mai hagun mai dama,
In hagun taƙ ƙiya ka koma dama,
Baba kilagon giwa mai jice daji shi ɗai!

Kai! Kai!

Wandara ko an laga,

Ana raga saura.

Sannu da yaƙi,

Waɗanda ka yi da bayi.

Ɓaleri sannu,

Mai hana ƙarya.

Duna ka nai da wa ka nai da aboki,

Kuma ka nai da ɗa ka nai da uba nai.

In ka ji ana faɗin mutum bai kwanto,
Bawa ba shi bauɗuwa bai kwanto,

Bai yi arangama da ɗan sababi ba!

Bai yi arangama da ɗan sababi ba!

Damben Jas Kwata ta yamma ga Bauchi,
Ɗan Abdu ya kashe Jaki,
Ya kashe mashi barwa,

Bai rage ko mutum guda ran nan ba.

Bai bar ko mutum guda sheda ba.

Kai bari damben Kano da yay yi riɓinji,
Yaƙi ya ci Ɗan Mutan Bakori,

Bai dawo da lafiya ga jiki ba!

Bai dawo da lahiya ga jiki ba!

Ja da baya ga rago,
Ɗan’anace ba tsoro ba,
Audu Kaiɗaigayya ya tahi Bakori,
Inda malammai nai,
Na dai koma Kano da ‘yag ganga ta,
Ban dai samu Kaikaɗaigayya ba,
Kuma na koma Kaduna mai buga kawo,
Ba mu dai iske Kaikaɗaigayya ba,
Kuma na dawo Gusau da ‘yan yara na,
Ba mu dai samu Kaikaɗaigayya ba.
Mutane ina Abdu za shi karya kumallo?
Huntuwa ‘yan maza ka sallas swahe,
Bilbil Abdu za shi karya kumallo.

Kai!

A buga waya ta zo Kano da Kaduna,
In ta zo, ta ce ma Audu ya dawo.
 
Makaɗan Bawa Ɗan’anace

Leave a Comment

Your email address will not be published. Required fields are marked *